Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
…
continue reading
Shiri ne da ke tattaunawa mai zurfi a kan batutuwan da suka shafi al'umma kai-tsaye, da nazari a kan tasirin da za su iya yi, da nemo hanyar magance ko kauce wa illolin da za su iya hifarwa bayan jin ta-bakin wadanda abin ya shafa.
…
continue reading

1
Kuskuren JAMB Da Ya Haddasa Faduwar Dalibai A Jarabawa
20:18
20:18
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
20:18Send us a text Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta yi amai ta lashe. Bayan ta musanta dukkan zarge-zargen da aka yi cewa tana da hannu a rashin kyawun sakamakon jarrabawar da ta shirya, Shugabanta ya fito ya amsa laifi. Yayin wata ganawa da ya yi da manema labarai, Farfesa Is-haq Oloyede ya ce dalibai 379,997 abin ya shafa, ku…
…
continue reading

1
Tasirin Mulkin Karba-Karba A Najeriya
26:48
26:48
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
26:48Karba-karba wani tsari ne da ya tanadi kewayarwar ludayi a tsakanin kudanci da arewacin Najeriya wajen rike shugabancin kasa. Manufar tsarin, wanda babu shi a Kundin Dokokin Najeriya, ita ce tabbatar da daidaito da haɗin kai da zaman lafiya a ƙasa. Sai dai yunkurin samar wa tsarin mazauni a ta yadda shugabanci zai rika kewaya a tsakanin shiyyoyi sh…
…
continue reading

1
’Yan Najeriya Sun Yi Tir Da Biyan Diyya Ga Kwastomomin Rukunin Band A
15:59
15:59
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
15:59Send us a text Wasu ’yan Najeriya sun yi Allah-wadai da wani umarni da Hukumar da ke Kula da Harkar Wutar Lantarki a Najeriya, wato NERC, ta bai wa kamfanonin rarraba wutar lantarki da su biya diyya ga abokan huldarsu da ke rukunin Band A. Hukumar ta NERC ta bai wa kamfanoni rarrabar wutar, wato DisCos, wannan umarni ne saboda rashin samar wa Band …
…
continue reading

1
Gaskiyar Tasirin Amfani Da Irin Noma Na GMO
25:25
25:25
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
25:25Send us a text Alamu na nuna cewa galibin manoma a Najeriya suna da shakku a kan amfani da irin da aka sauya ƙwayoyin halittarsa. Hakan dai na faruwa ne duk da bayanan da wasu masana suka yi game da alfanun wannan iri wanda ake kira GMO ko Genetically Modified Organism a turance. Tuni dai wasu masanan, waɗanda suka shirya wani taron bita ga manema …
…
continue reading

1
Abun Da Yasa Muka Ƙasa Kawo Karshen Tamowa A Wasu Jihohin Arewa Maso Gabas
25:33
25:33
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
25:33Send us a text Hukumomi a jihar Yobe sun dora alhakin kazancewar matsalar tamowa a kan rikicin Boko Haram da rashin shayar da jarirai nonon uwa yadda ya kamata da kuma gurbacewar harkar kiwon lafiya, da sauran su. Bayanin hakan na zuwa ne bayan ambato Babban Jami’i mai Kula da Ayyukan Jinkai na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya, Mista Mohamed Mali…
…
continue reading

1
Kalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyan 'Ya'yan Su
27:12
27:12
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:12Send us a text Duk wanda ya shekara arbain zuwa sama ya san irin tarbiyyan da ya samo daga wurin iyayen sa a da baya can, irin mu’amalan dake tsakanin sa da iyaye har ma da shakuwan dake tsakanin ‘ya’ya da iyaye. A yanzu kuwa abubuwa sun canza daga yadda aka san su, inda abubuwa suka rincabe sukayi wa iyaye yawa. Daya daga cikin manyan sauyin da ak…
…
continue reading

1
Boyayyun Dalilan Da Suke Sa Faduwa Jarabawa A Najeriya
23:18
23:18
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
23:18Duk shekara, dalibai kan rubuta jarabawa a matakai daban-daban na makarantu daban-daban. Daya daga cikin nau’ukan jarabawa da daliban Najeriya suke yi ita ce Jarabawar Sharen Fagen Shiga Manyan Makarantu, wato UTME. Kamar kowace shekara, a bana ma dalibai sun rubuta wannan jarabawa kuma a cewar Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB)…
…
continue reading

1
Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya?
27:16
27:16
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:16Send us a text Yin gwagwarmaya ko fafutuka wani abu ne da ke cikin jinin dan Adam, musamman idan yana kokarin ganin an samu sauyi ko cigaba a al'umma. Sai dai a Najeriya, sau da yawa ana danganta kalmar "gwagwarmaya" da rikici ko sabani da gwamnati. Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan yadda za a yi gwagwarmaya ba tare da an ta…
…
continue reading

1
Abin da ke kai matasan Najeriya ci-rani wasu ƙasashen Afirka
29:01
29:01
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
29:01Send us a text A ko’ina a Nahiyar Afirka za a iya samun ɗan Najeriya da ya bar ƙasar sa domin rayuwa a wata ƙasa. A yau ba sai an je Turai ko Amurka ba – kasashe irin su Mali, Ghana, Libya, Sudan da sauran su suna cike da matasa ’yan Najeriya wadanda suka je ci-rani. Shin me ya sa wadannan matasa suke barin Najeriya – uwa ga Afirka, mai albarkatu d…
…
continue reading

1
Yadda Naira Biliyan Daya Ta Salwanta A Gobarar Kasuwar Jos
23:58
23:58
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
23:58Send us a text Kusan Naira biliyan day ace aka kiyasta ta salwanta sakamakon gobarar da ta kone wane sashe na babbar kasuwar dake tsakiyar Jos babbar birnin jihar Filato. An rawaito cewar gobarar ta lakume shaguna fiye da dari biyar, galibinsu na masu sayar da kayan gwanjo. Mutane da dama dai sun rasa hanyar cin abincinsu, kasancewar galibinsu sun …
…
continue reading

1
Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta
24:51
24:51
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
24:51Send us a text Cututtuka da dama suna Kamari a Najeriya wanda a mafi yawancin lokuta ma wadanda ke dauke da irin wadannan cututtukan basu da masaniyar suna dauke da su. Kamar yadda majalisar dinkin duniya ta bayyana, zaman lafiya, rashin matsalar kwakwalwa, da samun wadata na daga cikin abubuwan dake tabbatar da lafiyar bil’adama. Wata cuta da ta a…
…
continue reading

1
Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
30:56
30:56
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
30:56Tatsuniya wata hanya ce ta ilmantarwa da bayar da tarbiyya da kuma koyar da al’adu da halaye na gari a tsakanin Hausawa. Tatsuniyoyi na ɗauke da darussa na rayuwa, suna kuma koya wa yara da manya jarumta da tausayi da sauran dabi’u kyawawa. Sai dai a yayin da duniya take sauyawa, ba kasafai matasa suke sha’awar sauraron tatsuniya ba. Wannan ne batu…
…
continue reading

1
Dalilin Karyewar Farashin Shinkafa A Wasu Kasuwannin Najeriya
23:31
23:31
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
23:31Send us a text Rahotanni suna nuna cewa farashin shinkafa, daya daga cikin nau’ukan abincin da ’yan Najeriya suka fi ci, ya karye a wasu sassan kasar. Sauyin farashin ya sa ana tambayoyi – shin me ya haifar da wannan sauyi? Kuma me hakan ka iya haddasawa a rayuwar talaka? A kan wannan sauyi da dalilansa ne shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai…
…
continue reading

1
“Dalilan Da Suka Sa Muke Sauya Sheƙa Zuwa Jam’iyya Mai Mulki”
25:12
25:12
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
25:12Send us a text Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da jijjiga sakamakon sauya shekar da ’yan siyasa daga banarori daban-daban suke yi. A baya-bayan nan tsallakawar da wasu jiga-jigan jam’iyyun adawa suka yi zuwa jam’iyyar APC mai mulki ta jawo diga ayar tambaya a kan dalilansu da kuma makomar hamayya a zaben 2027. Hakan dai yana faruwa ne a daidai lo…
…
continue reading

1
Dalilan Da Suka Sa Zazzabin Cizon Sauro Ba Ya Jin Magani
27:44
27:44
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:44Send us a text Zazzabin cizon sauro, wato malaria, na cikin cututtuka mafiya shahara da kuma hadari a Najeriya. Wani rahoton Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ya nuna cewa Najeriya na da kaso mafi girma na mace-macen da cutar take haifarwa a duniya. Sau da yawa wanda ya kamu da cutar ta malaria kan sake kamuwa da ita bayan ya warke. Ko me ya sa magung…
…
continue reading

1
Hanyoyin Amfani Da Kafafen Sada Zumunta Wajen Habbaka Kasuwanci
27:17
27:17
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:17Send us a text Tun zamanin kaka da kakanni ake gudanar da kananan sana’oi, wanda alumma ke dogaro dasu don biyan bukatun su na yau da kullum. Irin wadannan sana’oi sun hada da saka, jima, balangu, suyan kosai ko masa da dai sauran sana’oi da alumma keyi. A da can baya irin masu wadannan sana’a sun dogara ne da masu wucewa a bakin hanya don siyar da…
…
continue reading

1
Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
26:11
26:11
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
26:11Wutar lantarki ta zama tamkar gwal a wasu sassan Arewacin Najeriya, inda a wasu yankuna aka ba da rahoton samun sa’o’i biyu kawai a rana, wasu kuma ba sa samun ko daidai da dakika daya. Masu kananan sana’o’i suna kallon rayuwarsu da kasuwancinsu suna durkushewa yayin da kayan sana’arsu suke lalacewa saboda rashin wuta. Shirin Daga Laraba na wannan …
…
continue reading

1
Mene ne Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Kundin Tsarin Mulkin Najeriya?
27:04
27:04
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:04Send us a text Ko kun san tanadin da Kundin Tsarin Mulkin Kasa ya yi game da Ofishin Mataimakin Shuaban Kasa da ayyukansa da alhakin da ya rataya a wuyansa? Kundin na Tsarin Mulkin Kasa ne dai kundin dokoki mafi karfi a Najeriya wanda ya kunshi tanade-tanade a kan dukkan al’amuran da suka shafi alhakin da ya rataya a wuyan shuggabanni da ma al’umma…
…
continue reading

1
Me Ya Sa Matsalar Tsaro “Ta Gagari Gwamnati” A Najeriya?
26:02
26:02
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
26:02Send us a text A daidai lokacin da ake tunanin samun sauƙi daga ɗimbin matsalolin tsaro da na tada ƙayar baya a Najeriya, sai ga wasu matsalolin na ƙara Kunno Kai. Yayin da a wannan lokaci ake fuskantar kalubale iri-iri kama daga hare-haren da ake zargin na kungiyar Boko Haram ne a Arewa maso Gabas, zuwa ga sabbin kashe-kashe a wasu garuruwan jihoh…
…
continue reading

1
Sabbin Dabarun Hana Matasa Aikata Laifuffuka
25:36
25:36
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
25:36Send us a text Masu iya magana kan ce banza ba ta kai zomo kasuwa. Mai yiwuwa hakan ne ya sa matasan da ake zargi da aikata manyan laifuffuka shiga ofishin ’yan sanda, su kuma fita ba tare da wani ya harare su ba, balle ya kama su. ’Yan sandan dai sun ce wannan wata dabara ce ta yakar aikata manyan laifuka irin su sata da fashi da makami da kwacen …
…
continue reading

1
Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?
30:00
30:00
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
30:00Send us a text Doctor Zainab Muhammad na daya daga cikin mata a Arewacin Najeriya da ta jajirce tare da kudirin cika burinta na karantar kimiyya duk da kalubalen da wasu matan dake yankin Arewa suke bayyanawa suna fuskanta wurin karantar fannin. Doctor Zainab ba kimiyya kawai ta karanta ba, ta karanci daya daga cikin kimiyyoyin da ake ganin sun fi …
…
continue reading

1
Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo
23:01
23:01
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
23:01Duk wanda aka haifa ya tashi a kasar Hausa ya san al’adar nan ta bayar da ko karɓo ɗa ko ‘ya riƙo. A wasu lokutan mutum ne ke nema a ba shi rikon, a wasu lokuta kuma iyayen ne suke bayarwa don ƙashin kansu. Wannan alada ana yin ta ne da zimmar yauƙaƙa danƙon zumunci, amma a wasu lokuta kwalliya ba ta biyan kuɗin sabulu. Shirin Daga Laraba na wannan…
…
continue reading

1
Dalilan Rikice – Rikice A Jihar Filato
26:09
26:09
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
26:09Send us a text A yanzu haka, al’ummar jihar Filato na cikin fargaba da tashin hankali sakamakon jerin hare-haren da suka afku a wasu sassan jihar, inda daruruwan mutane suka rasa rayukansu, wasu kuma suka tsere daga muhallansu. Ko mene ne dalilin sake fitowar rikice-rikicen da suka dabaibaye yankin da ake ganin an fara samun zaman lafiya? Shirin Na…
…
continue reading

1
Dalilan "Farfaɗowar Boko Haram" A Jihar Borno
30:48
30:48
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
30:48Send us a text A yanzu haka al’ummar Borno na cikin zulumi sakamakon wasu hare-haren da ake zargin kungiyar Boko Haram ce ta kai a wasu sassan jihar. Wadannan hare-hare dai suna faruwa ne bayan shekaru da dama da ikirarin Gwamnati na cewa an yi nasarar nakasa kungiyar. Ko mene ne dalilin sake farfadowar kungiyar ta Boko Haram a wannan lokaci? Wanna…
…
continue reading

1
Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Za Ta Shafi Rayuwar 'Yan Najeriya
27:58
27:58
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:58Send us a text A Najeriya ana tafka muhawara a kan yadda farashin danyen man fetur yake kara faduwa a kasuwannin duniya. Wannan lamari dai ya haddasa damuwa a zukatan wasu ’yan Najeriya, kama daga masana tattalin arziki zuwa ga jami’an gwamnati, kasancewar danyen mai ne mafi muhimmanci a cikin hanyoyin samun kudin shiga. Sai dai tambayar da wasu ’y…
…
continue reading

1
Tasirin Da Dangantakar Yan Uwa Yake Ga Rayuwar Alumma
20:50
20:50
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
20:50Send us a text Irin dangantakar dake kasancewa tsakanin abokai na da matukar tasiri ga farin cikin wadannan abokai, ta yadda a wasu lokutan ma baka iya banbancewa tsakanin ‘yan uwan su na jini da kuma abokai. Irin wannan dangantaka ya kamata ne ace ana samun shi a wurin wadanda suke uwa daya uba daya ko kuma wadanda suke uba daya. Sai dai a yayin d…
…
continue reading

1
Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’
23:51
23:51
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
23:51Tun kaka da kakanni an san Hausawa da kawaici da kunya da kuma girmama na gaba da su. Mai yiwuwa wadannan dabi’u ne suka sa matar Bahaushe ba ta iya hada ido da mijinta, balle ta kira shi da sunansa na yanka. To amma a zamanin yau ba abin mamaki ba ne a samu matar aure ta kalli kwayar idon mijinta, ta kuma kira shi da sunansa na yanka. A kan wannan…
…
continue reading

1
Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu
24:01
24:01
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
24:01Send us a text A zamanin yau, ba kira da tura saƙo kawai ake yi da wayar hannu ba; baya ga haka, muhimmiyar hanya ce ta samun kuɗi da bunƙasa sana’o’i. Ko kun san dabarun amfani da wayoyinku don samun kuɗaɗen shiga? Idan ba ku sani ba, ko kuma kuna buƙatar ƙarin sani, ku biyo mu a shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci.…
…
continue reading

1
Mene Ne Tasirin NYSC Bayan Shekaru 50 Da Kafa Shi?
25:06
25:06
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
25:06Send us a text Shirin bautar ƙasa wanda aka kafa tun a shekarar 1973, an kirkire shi da nufin haɗa kan matasa daga kowane lungu da saƙo na ƙasar nan, domin fahimtar juna da kawar da wariyar yanki da kabilanci. Amma a yau, bayan shekaru fiye da arba'in da biyar da fara wannan shiri, jama’a da dama na tambaya: ko har yanzu shirin na da tasirin da aka…
…
continue reading

1
Dalilan Zuwan Mafarautan Arewa Kudancin Kasar Nan
30:11
30:11
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
30:11Tun bayan kisan mafarauta 16 dake hanyar su ta dawowa gida a garin Uromi dake karamar hukumar Esan dake jihar Edo ne dai al’umma da dama ke ta aikewa da sakon alhini ga ‘yan uwa da abokan arziki yayin da wasu kuma ke ta neman amsoshin tambayoyi game da lamarin da ya shige musu duhu. A yayin da wasu ke ganin a matsayin su na ‘yan kasa masu cikakken …
…
continue reading

1
Abubuwan Da Za Su Kwaɗaita Muku Azumtar Sitta Shawwal
24:06
24:06
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
24:06Send us a text Alqurani mai girma a cikin suratul Baqarah Allah ya wajabta wa musulmi da suka cika wasu sharudda azumtar watan Ramadana. Kamar yadda malamai suka sha fadi, wannan wata na dauke da wasu falala maras misaltuwa da bawa kan samu idan ya maida kai wajen ibada don samun rabauta daga ubangiji. Kazalika hadisai sun ruwaito kan falalar azumt…
…
continue reading

1
Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
24:02
24:02
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
24:02Send us a text Watan azumin ramadana kan zo da sauye sauye da dama da suka hada da kara kaimi wajen bauta wa ubangiji, samun lada ta hanyar ciyar da alumma da kuma falala masu yawa da basu misaltuwa. Wani sauyi da watan azumin watan ramadana ke zuwa dashi shine canjin yanayin ciman alumma, inda mutane ke canzawa daga cin abinci sau uku ko sama da h…
…
continue reading

1
Abubuwan Da Ya Kamata Musulmi Su Yi Gabani Da Ranar Sallah
27:32
27:32
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:32Send us a text Lokutan sallah kamar yadda aka sani lokacin ne na farin ciki, nuna godiya ga ni’imar da Allah yayi mana da kuma bauta. Kazalika lokacin ne da zamu lura da tabbatar da aiyukan da zamu aikata su zama ingattattu. Ko wadanne irin abubuwa ne mutane ya kamata su aikata kafin da kuma ranar sallah? Wadanne hanyoyi za a bi don tabbatar da zam…
…
continue reading

1
Halin Da Matasa Suka Tsinci Kan Su A Najeriya
24:45
24:45
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
24:45Send us a text Yau a Najeriya da yawa daga cikin matasa na fuskantar kalubale musamman wajen biya ma kan su bukatun su na yau da kullum sakamakon yanayin tattalin arzikin kasa, rashin aikin yi da kuma tsadar rayuwa. A wasu lokutan irin wadannan matasa sun yi karatu, wasu ma na da sana’oin su na hannu amma rashin aiki mai gwabi da zai biya musu buka…
…
continue reading

1
Yadda Farashin Kayan Masarufi Suke Gabanin Sallah
26:36
26:36
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
26:36A duk lokacin da aka ce lokutan bukukuwa sun karato, akan samu sauyi a dukkan alamura. Daya daga cikin irin wadannan sauyi da ake samu shine na farashin kayayyakin masarufi. A wasu lokuta, akan samu tashin farashin irin wadannan kayayyaki, a wasu lokutan kuma akasin haka. Shirin Daga Laraba na wannan makon zai tattauna ne kan farashin kayayyakin ma…
…
continue reading

1
Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Kasa Kiranye
30:12
30:12
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
30:12Send us a text Mulkin demokradiyya kamar yadda Hausawa ke cewa ‘yancin dan adam. A lokacin da ta baka damar tsayawa don a zabe ka kan wani mukami, kazalika ta baka damar zaben wanda kake so ya shugabance ka kuma ya wakilce ka. Wani abun da demokradiyyar ta baiwa alumma dama a kai kuma shine na yin kiranye ga wakilan da suka zaba musamman idan wadan…
…
continue reading

1
Yadda Kasuwanci Ke Kasancewa Gabani Da Cikin Ramadana
22:17
22:17
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
22:17Send us a text Hausawa sunyi gaskiya da suka ce ‘yawan mutane sune kasuwa’. Yawan hada hadar da ake yi tsakanin ‘yan kasuwa da abokan cinikin su na daya daga cikin abun da zai tabbatar maka kasuwanci na gudana kamar yadda ake so. Sai dai da Zarar ance watan Ramadana ya kama wasu daga cikin kasuwanci kan samu nakasu, inda wasu kuma ke samun habbaka.…
…
continue reading

1
Illar Sare Itatuwa Ga Canjin Yanayi Da Lafiyar Mu
30:13
30:13
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
30:13Send us a text Shekaru da dama kenan da hukumomin duniya ke gudanar da tarurruka da dama kan zakulo hanyoyin da za a kawo karshen dumamar yanayi a duniya. Dumama ko canjin yanayi na cigaba da barazana ga duniya, inda ake samun sauye sauye ga yanayi da wasu abubuwa da masana ke bayyana ka iya kara ta’azzara in ba’ayi wani abu a kai ba. Daya daga cik…
…
continue reading

1
Dalilan Da Ke Hana Wasu Teloli Cika Alƙawari
23:03
23:03
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
23:03Send us a text Sana’a na taka muhimmiyar rawa wajen habbaka tattalin arzikin alumma. Alumma da dama musamman a wannan lokacin na kara bayyana alfanun koyan sana’ar hannu don dogaro da kai maimakon dogara da aikin gwamnati ko na kamfani. Sai dai ana zargin wasu masu sana’ar hannu da rashin cika alkawari a wurin sana’ar su. Irin wadannan masu sana’ar…
…
continue reading

1
Abin Da Kundin Tsarin Mulki Ya Ce A Kan Ayyana Dokar Ta Ɓaci
27:18
27:18
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:18A karshe dai hasashen da wasu ke yi a Ribas ya tabbata, inda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-baci, ya dakatar da zababben gwamnan da mataimakiyarsa, da ma ''yan majalisar dokokin jihar. Sai dai bayan ayyana wannan doka da shugaban kasar ya yi 'yan Najeriya da dama suna ta bayyana ra’ayoyinsu kan wannan lamari. Yayin da wasu suke …
…
continue reading

1
Yadda Mai Karamin Karfi Zai Mallaki Muhalli Da Kudi Kalilan
27:23
27:23
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:23Send us a text Mallakan Muhalli na daya daga cikin burin kowanne dan Najeriya. Sai dai wannan buri a mafi yawan lokacin baya cika musamman ga masu matsakaitan samu. Kananan ma’aikata da mafi karancin albashin su yake naira dubu saba’in ba zai ciyar dasu, ko tufatar dasu ba, ballantana har suyi tunanin mallakan muhalli nasu na kashin kansu. Sai dai …
…
continue reading

1
Guraben Aiki Da Aka Kasa Cikewa A Najeriya
23:50
23:50
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
23:50Send us a text Duk da kukan rashin aikin yi da ako da yaushe ke cigaba da addabar ‘yan Najeriya, a wasu lokutan ba rashin aikin yi ne matsalar ba, wadanda zasu cike guraben ayyukan ne suka yi karanci a Najeriya. Alkaluma na cigaba da bayyana dubban ‘yan Najeriya ne dai ke fito wa daga manyan makarantun kasar a kowace shekara. A yayin da da yawa bas…
…
continue reading

1
Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
25:31
25:31
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
25:31Send us a text Rashin aikin yi na daya daga cikin manyan kalubalen da najeriya ke fuskanta a wannan lokaci, musamman la’akari da yanda ake cigaba da samun matasa dake da karfi a jika amma babu aikin yi. Hukumar kididdiga ta kasa ta fitar da bayanan dake baiyana cewa rashin aikin yi ya karu a najeriya da kaso 5.3 a farkon wannan shekarar, kazalika b…
…
continue reading

1
Ko Yarjejeniya Da ’Yan Ta’adda Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Arewa?
27:15
27:15
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:15Send us a text Masu iya magana kan ce dole uwar na ki. Matsalar tsaro da ta ki ci ta ki cinyewa musamman a Arewacin Najeriya tana tilasta wa wasu al’ummomi zakulo hanyoyin samun sa’ida ko yaya suke. Daya daga cikin wadannan hanyoyi da wasu al’ummomi suka runguma ita ce kulla yarjejeniya da ’yan bindigar dake addabar yankunansu. Shin ko cimma yarjej…
…
continue reading

1
Ko Kun San Asalin Tashe Da Tarihinsa A Kasar Hausa?
27:42
27:42
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
27:42Bayan dunbum falala, da yawan samuwar ibadun dake kara kusanta bayi ga ubangijin su, da azumin watan ramadana ke zuwa dashi kamar yadda malamai suka saba fada mana, Hakazalika Kuma a watan na Ramadan dai na zuwa da wata alada mai dimbin tarihi dake debe wa alumma musamman na arewacin Najeriya kewa. Wannan aladar itace ta tashe da ake fara yinta da …
…
continue reading

1
Abubuwan Da Suke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya
21:42
21:42
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
21:42Send us a text Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da daukar dumi yayin da ’yan kasa da dama suka yi kasake suna jiran girgiza ta gaba wadda wasu suke ganin tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya diga mata dan ba. A baya-bayan nan dai an yi ta tsegunguma da rade-radi a kana bin da wasu jiga-jigan ’yan siyasar kasar nan, musamman ’yan ad…
…
continue reading

1
Ladan Da Mai Aikin Karfi Yake Samu A Lokacin Azumi
25:59
25:59
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
25:59Send us a text Watan azumi lokaci ne da akan samu wasu ma’aikatu sun sassauta wa ma’aikata ta hanyar yi musu rangwame kamar rage musu yawan sa’o’in aiki. Sai dai a lokacin da wadannan mutane suke samun rangwame, akwai wadanda suke ayyuka ko sana’o’in da suka dogara da su ciyar da iyalansu. Sau da dama irin wadannan mutane sai sun fita sun yi aiki a…
…
continue reading

1
Falalar Bude Baki Cikin Iyali A Lokacin Azumi
26:50
26:50
Main Kemudian
Main Kemudian
Senarai
Suka
Disukai
26:50Send us a text Hadisi ya tabbatar da yadda cin abinci tare yake kara dankon zumunci da kaunar juna da albarka a tsakanin al’umma. Mai yiwuwa wannan ne ya sa akan samu Karin kusanci da shakuwa a tsakanin duk iyalan da kan zauna su ci abinci. Ko kafin watan azumi dai, wasu magidantan kan mayar da cin abinci tare da tare da iyalin su al’ada. Shin ko m…
…
continue reading