Usman Kabara awam
[search 0]
lebih
Download the App!
show episodes
 
Loading …
show series
 
Dakta Kamaluddeen Kabir, dan asalin jigar Katsina ne mai digirin digirgir wanda yayi karatunsa a tsakanin Najeriya da Birtaniya sannan kuma Malami ne yanzu haka a jami'ar Umaru Musa 'YarAdua da ke jihar ta Katsina. --- Send in a voice message: https://podcasters.spotify.com/pod/show/usmankabara/message…
  continue reading
 
Na'ima Idris Usman, cikakkiyar Likita ce da ke jihar Kanon Najeriya, ta yi karatun a tsakanin Najeriys da China. Ta bamu labarin rayuwarta daga kuruciya zuwa girmanta, da ma yadda aka yi ta fara ilimantar da mata ta kafafen sada zumunta game da lafiyar jikinsu duk da cewa furta kalmomin da ke da alaka da al'aura abu ne mai cike da kalubalen a kasar…
  continue reading
 
Usman Umar da aka fi sani da SojaBoy mawaki ne, dan wasan kwaikwayon zahirin rayuwa da ya fito a tauraron wani shirin wasan talbijin a Amurka mai suna 90DayFiance wanda ake bibiyar saurayi da budurwa don ganin yadda alakarsu ta soyayya ke tafiya.--- Send in a voice message: https://podcasters.spotify.com/pod/show/usmankabara/message…
  continue reading
 
Aisha Hassan matashiya ce 'yar asalin jihar Neja a Najeriya da ta girma a Ingila, sannan ta yi karatu mai zurfi a fannin hada-hadar kasuwanci. Bugu da kari ba a barta a baya ba wajen shiga fagen kafafen sadarwar zamani inda take koyar da salon sa sutura da daurin dan-kwali a shafukanta na yanar gizo. AISHA HASSAN: 'Yar Najeriya da Birtaniya gwanar …
  continue reading
 
An karrama Halima da lambar yabon gama digirin digirgir a matsayin dalibar da ta yi wa sa’o’inta fintinkau a fanni binciken sojojin garkuwar jikin bil’adama. Bugu da kari kuma sai ga wani babban kamfanin hada magunguna a duniya ya bata aiki sakamakon fahimtar amfanin abin da ta kware a fannin binciken kwayar halitta. --- Send in a voice message: ht…
  continue reading
 
Mu'awiya Said Abdullahi, ya yi karatu ne a fannin zanen gidaje da kuma tsara birane. An haifeshi ne a garin Kaduna, sannan iyayensa Lauyoyi ne. Ya fara digirinsa ne daga jami’ar Ahmadu Bello ta Zaria, ya kuma kammala a daya daga jami’o’in kasar Malaysia. Yayi digirinsa na biyu da na uku a Korea ta Kudu, inda yanzu haka ya ke aiki a matsayin shugaba…
  continue reading
 
Kaftin Ibrahim Sharif bakano ne dan Najeriya da ya bar gida tun yana dan saurayi zuwa Birtaniya domin aikin sa kai. Inda daga baya ya nausa Afirka ta Kudu inda ya cika burinsa na zama matukin jirgin sama, har ma ya buge da tsere keke a can. --- Send in a voice message: https://podcasters.spotify.com/pod/show/usmankabara/message…
  continue reading
 
Nura Abubakar dalibi ne da yake digirin digirgir a fannin Turanci da fasahar hotunan finafinan majigi. Matashin ya bayyana yadda jin wani shiri a gidan radiyon Muryar Amurka na VOA ya ba shi kaimin neman zuwa karatu a Amurka, har ya buge da koyar da harshen Hausa tun a digirinsa na biyu a wata jami'a ta Amurka.--- Send in a voice message: https://p…
  continue reading
 
Marzuq Ungogo wani hazikin matashin likitan dabbobi ne da yake digirin-digirgir a birtaniya, tare da yin binciken a fanni kwayoyin cututtukan dabbobin da kuma gano dalilan da ke hana wasu magungunan dabbobin aiki da ya kamata su yi. Ya bayyana mana tarihin rayuwarsa da ma yadda aka yi yayi digiri na biyu a Turai da ma ci gaba da digirinsa na uku. Y…
  continue reading
 
Karatu ne ya kawo iyayenta 'yan asalin jihohin Kano da Jigawa zuwa Amurka daga a Najeriya, amma kuma kaddarar zama ta kama su har suka hayayyafa. Iman ta fada min yadda take da burin zaman Najeriya duk kuwa da cewa a Amurka aka haifeta ta girma.--- Send in a voice message: https://podcasters.spotify.com/pod/show/usmankabara/message…
  continue reading
 
Maimuna Sulaiman Bichi da aka fi sani da ‘Yar Bichi ko Lolo’s Kitchen ‘yar asalin Najeriya ce ta suka dawo Amurka da zama tun tana shekaru 15 da haihuwa. Ta kuduri aniyar bude gidan abincin da zai kware a girke-girke musamman ma irin na gargajiyar Hausawa. --- Send in a voice message: https://podcasters.spotify.com/pod/show/usmankabara/message…
  continue reading
 
Binta Aliyu Zurmi da aka fi sani da Elbynt, ‘yar jarida ce daga Najeriya mazauniyar kasar Jamus kuma ma’aikaciya a daya daga fitattun gidajen radiyon Hausa da ke kasashen waje. Ku biyo mu don kallo ko sauraron tattaunawar da muka yi da ita game da tarihin rayuwarta a gida da kasahen waje. --- Send in a voice message: https://podcasters.spotify.com/…
  continue reading
 
An fi sanin Mohammed Ladan da sunan Dakta Ladan, sakamakon wani fitaccen shirin lafiya na gidan radiyon sashen Hausa na Muryar Amurka. Amma a likitance shi masanin kimiyyar hada magunguna ne wato ‘phamacist’. Dan asalin jihar Neja ne da ke Arewacin Najeriya, sannan a yanzu mazaunin Amurka fiye da shekara 40 tun bayan zuwansa karatu. --- Send in a v…
  continue reading
 
Bello Sheriff Sicqo haifaffen Maiduguri ne amma girman Kano a tarayyar Najeriya, wanda ya ci karo da kalubalen rayuwa a dalilin basirarsa ta waka wanda har korarsa daga gidansu aka yi. Amma maimakon ya saduda, sai ma ya tsalleke kasar zuwa Jamus a tarayyar Turai inda a yanzu haka yake zaune a matsayin mawaki kuma mai koyar da rawai. --- Send in a v…
  continue reading
 
Yusuf Alhassan dan asalin cikin birnin Kano ne da ya kwashe shekaru yana koyo da koyarwa a tsakanin Najeriya da Amurka game da ilimin fasahar sana’o’in hannu inda har ya taba zama zakaran gasar malaman koyar da sana’o’i ta Amurka. Malamin ya kuduri aniyarsa ta yadda zai taimaki Najeriya ta hanyar kai Kanawa 100 zuwa Amurka don koyon ilimin sana’a. …
  continue reading
 
Aliyu Mustapha Lawal bakano ne daga Najeriya wanda yake zaune a kasar Masira sannan ya shiga gasar kasidar larabci ta duniya mai taken Yariman Sha’iran Larabawa a birnin Abu Dhabi ta hadaddiyar daular larabawa. Ya tattauna damu game da rayuwarsa tsakanin Najeriya da Misira da kuma yadda aka yi ya sami shiga gasar larabawa a matsayinsa na bahaushe. …
  continue reading
 
Farfesa Abba na asibitin Mayo Clinic da ke Amurka, dan asalin jihar Kano ne a Najeriya da ya yi kaurin suna a Amurka, musamman a lokacin da ya shiga binciken yadda za a yi amfani da kwayar halitta ta stem cell a Turance wajen kirkirar maganin da zai iya sabunta halittar sassan jikin bil adama kamar zuciya da huhu ko bargo da makamantansu don yi wa …
  continue reading
 
Hauwa Mustapha Babura wacce ake mata lakabi da ‘Yar Babura sanadiyyar sunan garinsu Babura da ke jihar Jigawa a Najeriya, amma yanzu haka tana zaune a Amurka fiye da shekaru 30 wanda har ta zama ‘yar kasa. Mun tattauna da ita don ita don jin gwagwarmayar da ta sha kafin ta zama kwararriyar malamar makaranta a bangaren ilimin kananan yara da kuma ya…
  continue reading
 
Saratu Garba Abdullahi wacce aka fi sani da Saratitin Baba, ‘yar jihar Jigawa ce da ke Najeriya, amma yanzu haka a lokacin wannan hirar, tana karatun digirin-digirgir a wata jami’a da ke Amurka bayan ta gama digirin farko da na biyu a kasar Indiya a fannin aikin jinya da ungozoma da lafiyar mutanen karkara. Shiga cikin hirar don jin irin gwaggwarma…
  continue reading
 
Murtala likitan yara ne dan asalin jihar Adamawar Najeriya da ya rikide ya zama kwararren masanin lafiyar al’umma musamman mata da yara, wanda a yanzu haka ma’aikaci ne a wata kungiya mai zaman kanta da ta ke tallafawa harkokin lafiyar iyali a duniya ciki har da kasashen Afirka mai suna Pathfinder International da ke kasar Amurka.--- Send in a voic…
  continue reading
 
‘Yar Nijar kuma masaniyar kimiyyar ruwa da doron kasa da ke aiki a hukumar sama-jannatin Amurka ta NASA. Dakta Fadji Maina tana cikin wacce mujallar tereren arziki ta Forbes ta wallafa sunanta a cikin matasan duniya guda 30 ‘yan kasa da shekara 30 da suka sami nasara a rayuwa. Yanzu haka ma’aikaciya ce a hukumar sama jannatin Amurka ta NASA da ke a…
  continue reading
 
A shekarar 1984 a Najeriya an sami wani saurayi dan jihar Kano da ya fi kowane dalibi a Najeriya cin makin jarrabawar gama sakandaren kasashen Afirka ta WAEC a takaice. Yanzu haka dai wannan dalibin mai suna Sarki Abba Abdulkadir farfesa ne a bangaren haddasuwar cututtuka a Jami'ar Northwestern University da ke Chicago a Amurka. --- Send in a voice…
  continue reading
 
Adamu Hamza Bamalli ya sha gwagwarmaya a Najeriya a kokarin samun kyakkyawar rayuwa. To sai dai hakan ya zo masa da kalubalen rashin mahaifi tun yana dan karami wanda hakan ce sanadin kakarsu ya raine ahi tare da ‘yan uwansa. Bayan gama sakandare bai sami zuwa jami’a ba saboda wasu dalilai. Daga bisani kuma ya sami sanadin da ya fitar da shi daga N…
  continue reading
 
Imrana matashi ne danye shataf daga jihar Yobe, wanda har yanzu bai shekara talatin da haihuwa ba, sannan ba dan masu kudi ko mulki ba ne, amma ya sami nasararorin rayuwar da har Sarauniyar Ingila sai da ta karrama shi saboda wasu dalilan da matashin ya bayyana a wannan tattaunawa da mu ka yi dashi game da tarihin rayuwarsa.--- Send in a voice mess…
  continue reading
 
Halima Djimrao tsohuwar ma’aikaciyar sashen Hausa na Muryar Amurka, ta yi doguwar hira game da rayuwarta tun daga haihuwa har zuwa girmanta da karatunta na addini dana zamani, da ma yadda aka yi ta sami aiki a Muryar Amurka da ke birnin Washington DC da kuma dalilin yin ritayarta a lokacin da duniyar aikin radiyo ke yayinta.--- Send in a voice mess…
  continue reading
 
Na ziyarci daya daga cikin kwararrun likitocin a Amurka dan asalin Najeriya da ya kware a fanni hanji da matsarmama da kuma cutar daji. Likita Sabo Tanimu ya bani labarin yadda ya taso a garin Makurdi, har zuwa dawowarsa Amurka da kuma yadda ya kwashe shekaru a Amurka amma hakan bai hana shi kafa gidauniyar taimakon al’ummar da ya fito ba a Najeriy…
  continue reading
 
A cikin wannan hirar ne mawaki kuma dan wasan barkwanci sannan Sarkin Samarin Turai mai suna Haruna Salisu da aka fi sani da Chizo1 Germany, ya fada mana tarihin rayuwarsa tun daga Najeriya zuwa shigarsa Turai a matsayin dan gudun hijira ta hanyar keta sahara da teku har da yadda ya tsinci kansa a kasar Jamus inda ya buge da auren Bajamushiya. --- …
  continue reading
 
Ni Usman Kabara na kirkiro shirin nan ne don in dinga zakulo Hausawan da suka yi fice ko nasara a fannoni daban-daban a fadin duniya domin jin irin gwagwarmayar da suke sha kafin kai wa ga gaci, don hakan ya zama jagorar tinkarar rayuwa ga matasanmu. Ku lalubi shirin tare da danna 'subscribe' ko 'follow' a radiyon tafi da gidanka internet a tsarin …
  continue reading
 
Loading …

Panduan Rujukan Pantas

Podcast Teratas